Kungiyar yankasuwar rimi dake nan jihar Kano ta jaddada goyan bayanta ga Gwamnatin jihar Kano domin Samar da cikakken tsaro da dakile shaye shayen muggwan kwayoyi da kwacen wayoyin alumma.
Shugaban Kungiyar saidu salisu ne ya jaddada hakan a lokacin da yake zantawa da Manama labarai a ofishin Kungiyar dake kasuwar.
Yace Kungiyar ta kafa kwamati da zai rika tabbatar da tsaron lafiya da dukiyoyin alummar kasuwar da kuma Baki da suke shigowa domin yin siyayya.
Shugaban Kungiyar Alh saidu salisu ya bukaci hukumomi da Gwamnatoci a matakai daban daban da su tallafawa Kungiyar sakamakon irin gudunmawar da take bayarwa da hadin Kan jami’in tsaro na ofishin yansanda na shahuci da sauran jami’in tsaro na sa Kai.
Saidu salisu yace harkokin Samar da tsaro ba na jami’in tsaro kawai bane,har ma da sauran kungiyoyin alumma, saboda abin ya shafi bangaren da dama a fadin jihar Kano.
Ya bayyana cewar Kungiyar kasuwar rimi ba za ta gajiya ba wajen taimakawa yunkurin Gwamnatin jihar Kano na tabbatar da cikakken tsaro, domin zaman lafiya shi yake baiwa damar ci gaba da kawunansu Yadda yakamata.
Shugaban Kungiyar yayi Kira ga Gwamnatin jihar Kano da ta tallafawa Kananan yankasuwa da Basu da jarin da gudanar da kasuwancinsu na yau da kullum, Inda yace babban matsalar Kananan yankasuwa shine rashin jarin da za su habaka kasuwancinsu.
Alh saidu salisu ya shawarci yankungiyar da su kasance masu baiwa shugabancin Kungiyar cikakken hadin Kan daya kamata domin ciyar da alummar kasuwar da kasuwancinsu gaba.










