Majalisar wakilai a ranar Talata ta yi zargin cewa shigowa aka yi da ƴan ƙunar baƙin wake mata da suka tayar da bam a jihar Borno.
Ƴan ƙunar bakin waken dai sun tayar da bama-baman ne a garin Gwoza a ranar Asabar inda suka kashe mutane fiye da 30.
Ƴan majalisar sun bayyana haka ne bayan la’akari kan ƙudirin gaggawa da ɗan majalisa mai wakiltar Gwoza/Chibok/Damboa, Ahmed Jaha ya gabata.
Yayin da yake Allah wadai da harin, Ahmed Jaha, ya bayyana cewa bincike ya nuna cewa ƴan ƙunar baƙin waken shigo da su aka yi.
Ya bayyana cewa ƴan ta’addan an ɗauko hayarsu ne, aka sauya musu tunani tare da shigo da su daga wajen jihar domin kai harin ƙunar baƙin waken a Gwoza,
Rahoton Daily Post ya tabbatar da cewa Harin ya jawo rasa rayukan mutane Sama da 30 yayin da wasu da dama suka samu raunuka.
Ɗan majalisar ya bayyana cewa tayar da bama-baman ya ƙara fito da barazanar ayyukan ta’addanci da ƙasar nan ke fuskanta.










