Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ɗaukar dawainiyar samar da ingantaccen ilimi a Najeriya yafi karfin gwamanti ita kadai
Saboda haka ta bukaci kungiyoyi da masu abin hannu su tallafawa gwamanti wajen samar da ilimi mai inganci a fadin Najeriya
Ministan ilimi, Farfesa Tahir Mamman ne ya fadi haka yayin taron karrama Dakta Emeka Offor da matarsa Dakta Adaora Offor
Mamman ya ce gwamnatin tarayya na kashe mukudan kudi kan ilimi amma idan dambu ya yi yawa bai jin mai.
Saboda haka ya bukaci kungiyoyi da masu hannu da shuni su kawo agaji domin tallafawa harakar ilimi yana mai cewa haka ne kawai zai samar da ingantaccen ilimi a Najeriya.
Kazalika ya bukaci yan Najeriya su yi koyi da Dakta Emeka Offor wajen tallafawa ilimi a Najeriya.
Dakta Emeka ya ba jami’ar Najeriya ta UNN da jami’ar Nnamdi Azikiwe NAU kyautar N100m da N50m domin gudanar da ayyukan yadda ya kamata.











