‘YAN MAJALISUN TARAYYA SUN KOKA WAJAN RASHIN BAWA SASSAN DASUKE KARKASHIN MA’AIKATAR MAN FETUR KULAWA TA MUSAMMAN A KASAFIN KUDIN SHEKARA TA 2024.
Wannan koke Yafito daga bakin Jagoran ‘yan majalisun da suka fito daga Arewacin Najeriya, Kuma Shugaban Kwamitin dake kulada Ma’aikatar Man Fetur na Majalisar Wakilai Hon, Alhassan Ado Doguwa,
Alhassan Ado yayi wannan kokene Jim kadan bayan kammala zaman Hadaka na Majalisun Tarayya ta Dattawa da Wakilai na Kwamitin dake kulada kasafin Kudi na Ma’aikatar Man Fetur.
Ado Doguwa yace duk da kasancewar Shugaban kasa shine Babban Minista na Ma’aikatar Man Fetur, kasafin Kudi na Ma’aikatar bai wuce Naira Biliyan 10 ba.
Dan majalisar yakara da cewa, duk da kasancewar Ma’aikatar Man Fetur ce take da alhakin aikin gano inda ake tsammanin samun Man Fetur, Kuma Ma’aikatar ce take da Alhakin gaiyato masu saka Hannun Jari daga Kasashen Waje a fangaren Man Fetur da kuma kulawa da Matatun Man dake Kasarnan.
A Karshe, Hadakar Majalisun sunyi kira ga Fangaren Zartarwa da duba na Musamman akan cire Tallafin Man Fetur domin Canjawa ‘Yan Najeriya ta wani fangaren domin samun Saukin Rayuwa.
Wacca Shawara zaka bayar akan wannan kokene?












