Anja hankalin Al’ummar musulmi musamman mata dasu jajirce wajen addu’a tare da kan kan dakai ga majalicci domin neman yafyewarsa bisa halin da aka tsinrci kai da gyaran zukatu baki daya
Kiran ya fito ne daga bakin shugabar kungiyar mahakiratu illallah malama zainab isah gambo a yayin taron addu’ar da suka shirya a fadar maimartaba sarkin kano.
Malama Zainab isah Gambo ta bayyana taron addu’ar da kungiyoyin Tijjaniyya da dai daikun mata su ka gudanar da cewa itace mafita Kuma hanya mafi dacewa da zata saukaka lamuran da suka shafi Al”umma musamman yanayin tsadar da ta addabi mutane.
Shugabar mahakiratu illallah Kuma jagorar da”irar zikiri a bangaren mata a masarautar kano tace sun ware ranar ne domin Kai kuka ga mahalicci domin shine Mai yaye duk wata damuwa da taimakon masu girma iyalin maimartaba sarkin kano mallam muhammadu sunusi na biyu.
Malamar tace aduk sanda al’umma suka tsinci kansu a wani yanayi ya zama wajibi suyi koyi da magabata (sufaye) domin sune masu tsantsar Mika wuya ga mahalicci ta fannin Kai kokenmu ga Allah S W A Kuma Ana samun nasara don haka take kiran muyi koyi dasu .
Shugabar mahakiratu illallah ta CE fatansu shine su rubanya kokarinsu wajen yiwa jihar kano dama kasa baki daya addu’ar neman sauki daga halayen da ake ciki
kungiyoyin Tijjaniyya dukka sun halacci taron addu’ar Wanda duk shekara ake ware Rana guda domin addu’ar kungiyoyin sun hadar da Quddamu Rasulillah, da inuwar matan Tijjaniyya da Kuma daukakin zawiyya .












