Minna, jihar Neja – Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, a ranar Litinin, ya ziyarci tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (mai ritaya).
Tinubu ya bar wurin bikin kaddamar da aikin da Gwamna Mohammed Umaru Bago ya aiwatar a Minna, babban birnin jihar Neja, ya wuce kai tsaye zuwa gidan IBB.
ya kai ziyarar aiki ta kwana ɗaya jihar Neja a ranar Litinin 11 ga watan Maris, domin kaddamar da aikin sabunta ginin filin jirgin sama a Minna.
Kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito, an canza sunan filin sauka da tashin jirgin saman zuwa filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu na ƙasa da ƙasa.
Bayan kaddamar da wannan aiki, shugabam ƙasa Tinubu ya kuma yi wasu ayyukan duk a jihar Neja da ke Arewa ta Tsakiya.
An tattaro cewa shugaba Tinubu ya kai ziyara tare da shafe sama da sa’a guda yana tattaunawa IBB kan batutuwan da suka shafi halin da kasar nan ke ciki.












