Kungiyar Matuka motocin haya ta kasa reshen Tashar Malam Kato,ta bayyana irin kalubalen da ‘ya’yanta suke fuskanta a sakamakon cire tallafin man fetur da aka yi a fadin kasar nan.
Ma’ajin Kungiyar Alh.Samaila Giredy ne ya bayyana haka a lokacin da yake yiwa manema labarai Karin haske dangane da halin da suke ciki a wannan lokaci.
Yace, Direbobi da dama suna mutukar shan wahala sakamakon tashin gwauran zabi da man yayi a kasar nan, inda yace, maimakon man fetur din Dubu goma (10000)da direbobi suke sha zuwa Abuja a lokacin baya, yanzu dole sun sha na naira dubu arbain,Wanda duk kudaden da suka samu yana karewa ne a kudin mai.
Samaila yace,baya ga tsadar mai,akwai rashin kyan hanyoyi da ake fama da su da barayi da jami’an da suke Addabar Direbobin akan hanya daga nan jihar kano zuwa babban birnin tarayya Abuja.
Alh Samaila yayi kira ga Gwamnatoci a matakai daban daban da su taimakawa Direbobin motocin haya duba da halin da suke fuskanta na matsin rayuwa,Wanda duk yana karewa ne akan Talakawa yake karewa.
Daga karshe yayi kira ga’ya’yan Kungiyar Direbobin motocin haya da su kwantar da hankulansu domin Kungiyar ta himmatu wajen ganin ta kawo karshen matsalar dake faruwa a bangarori daban daban da kungiyar ke fuskanta.
Ibrahim sani gama pyramid radio












