Tsohuwar hadimar Muhammadu Buhari, Lauretta Onochie, ta caccaki gwamnati mai ci ta Shugaban kasa Bola Tinubu
Yayin da ake fama da tsadar rayuwa a kasar nan, Onochie ta zargi gwamnatin Tinubu da kin daurawa daga inda tsohon ubangidanta ya tsaya
Ta bayyana hakan ne a shafinta na sada zumunta inda, ta tambayi inda shinkafa iri-iri da aka samar gwamnatinsu kamar su ‘Lake Rike, Ebonyi Rice’ da
Lauretta Onochie, tsohuwar hadimar tsohon shugaban kasa Buhari kuma tsohuwar shugabar hukumar NDDC, ta garzaya shafinta na soshiyal midiya don tambayar inda shinkafar da ake yi a gwamnatin ubangidanta suka shiga.
A wani rubutu da ta yi a ranar Litinin, 12 ga watan Fabrairu, ‘yar siyasar haifaffiyar Niger Delta, ta zargi gwamnati mai ci karkashin Tinubu da rashin ci gaba daga inda aka tsaya.
Ta tambayi abin da ya faru da shinkafar ‘Lake Rice’, shinkafar ‘Ebonyi Rice’ da wasu da dama bayan ta wallafa hotunansu a shafin nata.
Ta rubuta: “Me ya sa muke guje wa ci gaba? Me ya faru da shinkafar ‘Lake Rice’, ‘ Ebonyi Rice’, da dai sauransu?”
Yadda ‘Lake Rice’ ta yi battan dabo Shinkafar ‘Lake Rice’ na daya daga cikin abubuwan da aka samar daga manufar habbaka noma ta gwamnatin Buhari.
An samar da shi ne ta hanyar hadaka tsakanin gwamnatin Legas da Kebbi.
Kamar yadda jaridar The Guardian ta ruwaito, shinkafar ta bace sosai a lokacin kullen shekarar 2020 a Legas. Shekaru biyu da fara ta, shinkafar ta bace a kasuwa bayan wata yarjejeniyar fahimtar juna ta noma da gwamnati ta sanya wa hannu.
Ba a magance matsalar ba har sai da Ambode ya bar ofis a ranar 29 ga Mayu.












Hmmm waikurace zatace dakare maye Allah dai yasauka kamana Ameen amma Al uma nacikin wani hali marar dadi