Tsohon gwamnan jihar Bauchi, Isa Yuguda, ya ce wasu gurbatattun ‘yan siyasa ne suka haifar da faduwar darajar Naira a kasuwar duniya
Ya yi ikirarin cewa ‘yan siyasar na kwashe daloli suna ajiyewa a gidajensu da kuma asusu na kasashen waje kawai don son kan su
Isa Yuguda ya kuma yi nuni da cewa rashin tsaro na daga cikin abubuwan da ke haifar da matsalar karancin abinci da kasar ke fuskanta
Ya kuma ce daya daga cikin abubuwan da ke haifar da matsalar karancin abinci da kasar ke fuskanta shi ne rashin tsaro, tare da kuma boye kayan abinci da ‘yan Najeriya ke yi.
Yuguda ya bayyana haka ne a wajen taron magance talauci a Arewacin Najeriya da kungiyar Arewa New Agenda, ANA ta hada a karshen mako a Abuja.
A cewar tsohon gwamnan, magance fatara da talauci a Arewacin Najeriya na bukatar daukar matakan da suka dace, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.
Ya yi kira ga tawagar tattalin arzikin gwamnatin Shugaba Tinubu da su fito da tsare-tsare da za su magance kalubalen tattalin arzikin kasar nan.
Ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta duba sosai tare da saka hannun jari a fannin tsaro domin tunkarar kalubalen tsaron da kasar nan ke fuskanta a halin yanzu.
Da yake karin haske game da janye tallafin man fetur, tsohon gwamnan ya ce ya zama dole saboda yadda ake tafka almundahana a harkar man fetur.












