Jirgin saman samfurin E-120, mallakar kamfanin jiragen sama na Halla Airlines ya taso ne daga birnin Garoowe na yankin Puntland na Somaliya zuwa filin jirgin saman Aden Adde na Mogadishu ya hadu da iftila’i na hadari a kan hanya.
Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta kasar Somaliya tace an sami nasarar tserar da dukkan fasinjoji 30 da ma’aikatan jirgin su hudu.
“Babu rasa rayuwa a hadarin sai dai kananan raunuka,” in ji hukumar SCAA a cikin wata takaitacciyar sanarwa. “Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen saman ta Somalia ta tabbatar da cewa za’a fitar da rahoton farko a kan hadarin da zarar an kammala binciken da ake yi a yanzu.”
Hotunan da aka yadda ta talabijin ya nuna jirgin ya kauce daga titin tashi da saukar jirage ne nan take bayan ya sauka.
Matukin jirgin bai bayar da rahoton wata matsala ba ga hasumiyar kula da zirga-zirgar jiragen sama kafin faruwar lamarin.
Ismail Mohamud na kamfanin jiragen sama na Halla ya shaidawa Muryar Amurka cewa daga baya za’a fitar da rahoton sakamakon binciken.
Alamu na farko sun nuna cewa mai yiwuwa kuskuren matukin jirgin ne ya haddasa hadarin, a cewar wani jami’in Somaliya da ya bukaci a sakaye sunansa.
Ya kara da cewa “Za a tabbatar da gaskiyar lamarin da zarar an yi nazarin na’urar nada murya da akwatin bayyana bincike na cikin jirgi.”
Hukumomin filin tashi da saukar jiragen sama na Somalia sun inganta ayuka a cikin ‘yan shekarun nan, inda suka sake karbe ikon zirga-zirgar jiragen sama daga Majalisar Dinkin Duniya. A farkon wannan shekarar, Somaliya ta dawo da matsayinta na ajin farko daga kungiyar sufurin jiragen sama ta kasa da kasa.
Jirage sama da 150 na cikin gida da na ketare ne ke amfani da filin jiragen sama na Mogadishu a kullum, a cewar hukumar kula da filayen jiragen sama. Manyan kamfanonin jiragen sama na kasa-da-kasa da ke amfani da filin jirgin sun hada da Turkish Airlines, Qatar Airways da Ethiopian Airlines.











