• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Wasu fasinjojin jirgin sama sun sha da kyar bayan sun hadu da hadari

aksam by aksam
July 13, 2023
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
469
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Jirgin saman samfurin E-120, mallakar kamfanin jiragen sama na Halla Airlines ya taso ne daga birnin Garoowe na yankin Puntland na Somaliya zuwa filin jirgin saman Aden Adde na Mogadishu ya hadu da iftila’i na hadari a kan hanya.

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta kasar Somaliya tace an sami nasarar tserar da dukkan fasinjoji 30 da ma’aikatan jirgin su hudu.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

“Babu rasa rayuwa a hadarin sai dai kananan raunuka,” in ji hukumar SCAA a cikin wata takaitacciyar sanarwa. “Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen saman ta Somalia ta tabbatar da cewa za’a fitar da rahoton farko a kan hadarin da zarar an kammala binciken da ake yi a yanzu.”

Hotunan da aka yadda ta talabijin ya nuna jirgin ya kauce daga titin tashi da saukar jirage ne nan take bayan ya sauka.

Matukin jirgin bai bayar da rahoton wata matsala ba ga hasumiyar kula da zirga-zirgar jiragen sama kafin faruwar lamarin.

Ismail Mohamud na kamfanin jiragen sama na Halla ya shaidawa Muryar Amurka cewa daga baya za’a fitar da rahoton sakamakon binciken.

Alamu na farko sun nuna cewa mai yiwuwa kuskuren matukin jirgin ne ya haddasa hadarin, a cewar wani jami’in Somaliya da ya bukaci a sakaye sunansa.

Ya kara da cewa “Za a tabbatar da gaskiyar lamarin da zarar an yi nazarin na’urar nada murya da akwatin bayyana bincike na cikin jirgi.”

Hukumomin filin tashi da saukar jiragen sama na Somalia sun inganta ayuka a cikin ‘yan shekarun nan, inda suka sake karbe ikon zirga-zirgar jiragen sama daga Majalisar Dinkin Duniya. A farkon wannan shekarar, Somaliya ta dawo da matsayinta na ajin farko daga kungiyar sufurin jiragen sama ta kasa da kasa.

Jirage sama da 150 na cikin gida da na ketare ne ke amfani da filin jiragen sama na Mogadishu a kullum, a cewar hukumar kula da filayen jiragen sama. Manyan kamfanonin jiragen sama na kasa-da-kasa da ke amfani da filin jirgin sun hada da Turkish Airlines, Qatar Airways da Ethiopian Airlines.

Share188Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Yadda sanata Lado Danmarke ya gwangwaje wasu mazabu da ayyukan ci-gaba

Next Post

Daurawa ya bayyana matakai da irin kayan Dakin da zasu rabawa zawarawa da yanmata bayan Hizba ta d’aura musu Aure

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Il Futuro del Gioco Digitale in Italia: Innovazioni, Tendenze e l’Esperienza Interattiva

April 21, 2025
Kali adadin maniyyata aikin Hajji na kowacce jiha a Najeriya

Kali adadin maniyyata aikin Hajji na kowacce jiha a Najeriya

April 3, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media