Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya ce hadiman da tsohon shugaban ƙasa, Muhamnadu Buhari, ya kewayen kansa da su sun illata Najeriya.
Sanata Sani ya yi iƙirarin cewa waɗanda Buhari ya aminta ya naɗa a muƙamai sun yi kashe mu raba da dukiyar baitul mali kuma sun gurgunta makomar ƙasar.
Ya bayyana haka ne ranar Laraba, 31 ga watan Janairu, 2023 a wurin tattaunawar da Legit.ng ta shirya ‘Twitter Space’ mai taken, “Yaƙi da rashawa ko matsalar tsaro: Mafi muhimmanci ga FG a 2024.
Ya kuma yi iƙirarin cewa shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gaji tulin bashin da ya kai na N77tr daga Buhari, wanda shi ya haifar da matsalar tattalin arzikin da aka shiga.












