An yi kira ga gwamnatin jahar bauchi ta dakatar da makarantun da ba su cika doka da kaidojin koyarwa ba.
Kiran ya fito ne ta bakin Magatakadda na makarantar Aminu sale college of education dake azare, Abdullahi babbaji a yayin ganawarsa da manema labarai a ofishinsa.
Babbaji yace akwai makarantun da Bai kamata su koyar ba Sama da mutum hamsin a fadin jahar ta Bauchi ba.
Sannan Magatakadda ya Kuma ce akalla akwai kimanin kwasa kwasai Sama da goma Sha biyar Kuma a ciki akwai darussan da dalibi zai Iya dogara da kansa ba sai ya jirayi gwamnati ta bashi aikin yi ba,
Abdullahi babbaji ya Kuma godewa gwamnatin jahar bauchi karkashin jagorancin sanata Bala Abdulkadir kauran bauchi bisa hadin Kai da goyan bayan da yake Bawa makarantar, daga karshe ya bukaci aluma masu hannu da shuni dasu rika kokarin tallafawa matasa da tallafin karatu musammama a wannan makaranta











