Hukumomin Najeriya sun bayyana cewa ayyukan yan damfara na yanar gizo da aka tarwatsa suna ƙara girma, inda suke da ofisoshi cike da kwamfutoci, da dubban SIM, kuma suke bayar da horo ga wasu ‘yan Najeriya da ake dauka don gudanar da damfara.
Hukumar Interpol ta ce yaduwar amfani da wayoyin salula ya kara sa ‘yan Afirka cikin hadarin damfara, inda kusan kashi 30% na laifuka a Yamma da Gabashin Afirka suka shafi yanar gizo. Haka kuma, kasashen Afirka da dama har yanzu suna gina dokoki da tsare-tsare don yaki da laifukan yanar gizo.
Shugaban EFCC, Ola Olukoyede, ya ce kama ‘yan kasar Sin 148 da aka yi a karshen shekarar 2024 ya nuna Najeriya na daukar mataki mai tsanani wajen yaki da laifukan yanar gizo, yana mai cewa wasu baƙi na amfani da munanan suna da Najeriya ta samu don kafa tushen ayyukan su na laifi.












