Kungiyar masu siyar da magunguna ta jihar Kano ta jaddada kudurin ta na hada hanu da gwamnatin jihar domin tsaftace harkar ta hanyar hana shigo da miyagun kwayoyi.
Shugaban kungiyar Muhammad Misbahu64d Yahya shine ya jaddada wannan kudiri a zantawar sa da manema labarai a ofishinsa dake birnin kano.
Shugaban yace a matsayin su yan asalin Jihar Kano dole ne suyi duk mai yuwuwa wajen bawa gwamnati gudun mawa musamman a sha’anin da ya shafi sana’ar su ta magunguna.
Da yake tsokaci akan batun komawar yan kasuwar su filin kasuwar Dan gwauro yace dama shiri ne na wasu daga cikin mukarraban gwamnatin da ta shude ta Dacta Abdullahi Umar Ganduje.
Yace yawan masu siyar da magani a jihar Kano sun haura mutum 20,000 amma wacccen kasuwar da ake cewa su koma gaba daya rumfunan ta 600 ne
A cewar sa a don haka ne suka garzaya gaban kotu domin ta samar musu da mafita
Daga karshe ya ja hankalin yan kasuwar su da suyi kokari wajen kauce shiga cikin harkar taammjli da miyagun kwayoyi.











