Daga Hassan Umar Gwammaja
Kafar watsa labaran Koriya ta Arewa ta ce shugaban ƙasar, Kim Jong Un, ya kai ziyara ɗaya daga cikin yankunan da aka yi mummunar ambaliyar ruwa da mahaukaciyar guguwa.
Rahotanni na cewa an ga yadda shugaban yake tsara yadda za a kwashe mutanen yankin da yawansu ya kai dubu 15, zuwa babban birnin ƙasar tare da sake gina sababbin gidaje a inda lamarin ya faru.
Sai dai hukumomin ƙasar ta Koriyar ta Arewa ba su bayar da rahoton yawan mutanen da suka mutu ko suka jikkata ba, illa dai kafar watsa labaran ƙasar ta bayyana lamarin da mummunan hadari.









