Cif Olusegun Obasanjo ya gargaɗi gwamnatin tarayya ta biya bukatun matasa masu zanga zanga saboda suna kan gaskiya
Tsohon shugaban kasar ya ce Najeriya ta samu koma baya bayan ya bar mulki saboda waɗanda suka biyo bayansa ba su yi abin da ya dace ba
Obasanjo ya bayyana haka ne yayin da ya karɓi bakuncin ƴan majalisar wakiali shida a gidansa da ke Abeokuta a jihar Ogun
Daily Trust ta ce ƴan majalisar sun buƙaci rika karɓa-karɓa tsakanin Arewa da Kudu, sannan kujerar gwamna ta rika kewaya wa tsakanin mazaɓun sanatoci uku a kowace jiha.
Yan majalisar dai sun gana da Obasanjo ne ƙarƙashin jagorancin Hon. Ugochinyere Ikenga mai wakiltar mazabar Ideato ta Arewa da Ideato ta Kudu a jihar Imo.
A jawabinsa, Obasanjo ya ce gwamnatocin da suka shuɗe sun sauka daga kan tubalin da ya kafa a lokacin mulkinsa, yana mai cewa hakan ya jawo koma baya.











