Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya hangen sa inda yace ya hango babban haɗari na tunkaro Najeriya idan har ba a magance matsalar ƴan bindiga ba
Shugaban kasar ya ce burin haɗa tattalin arzikin dala tiriliyan ɗaya ka iya shiga babban haɗari idan jami’an tsaro ba su yi da gaske ba
Tinubu ya yi wannan furuci ne a taron bada bayanai kan yanayin tsaron ƙasa da ya gudana a Aso Villa ranar Jumu’a
Ya yi wannan jawabi ne ga hafsoshin tsaro da shugabannin hukumomin tattara bayanan sirri a taron ba da bayanai kan harkokin tsaro a Villa, Abuja ranar Jumu’a.
FCT Abuja – Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci hukumomin tsaron Najeriya su ƙara matsa kaimi kuma su gaggauta kakkaɓe ƴan bindigan da suka addabi jama’a.
Bola Tinubu ya yi gargaɗin cewa burin Najeriya na haɗa tattalin arzikin dala tiriliyan ɗaya zai shiga babban haɗari idan har matsalar ƴan bindiga ta ƙi ƙarewa.









