• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Shirin Gwamnatin Kano Na Kula Da Lafiyar Baki Ya Amfanar Da Mutane sama da 15,000

Khadija Maitaya by Khadija Maitaya
July 22, 2026
Reading Time: 1 min read
0
Home LAFIYA
ADVERTISEMENT
471
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Mutane fiye da dubu 15 a kananan hukumomi 22 na Jihar Kano sun amfana da shirin duba lafiyar baki da hakora da ba da magani kyauta a karkashin shirin kula da lafiyar baki da gwamnatin jihar take daukar nauyi.

Babban jami’i Mai Kula da Lafiyar Baki na Hukumar Kula da Lafiyar Farko ta Jihar Kano, ‘Therapist’ Nura Aliyu Sa’id, ne ya bayyana hakan a cikin shirin Radio Kano mai suna _’Yau da Gobe’.

RelatedPosts

Cutar mashako

Governor Yusuf commissions Kano center for disease control

An Kama Wata Matashiya Mai Shekaru 27 Bisa Zargin Satar Jariri A Asibiti A Zamfara

Ya ce ayarin likitocin hakori na zagayawa zuwa garuruwa domin duba lafiyar hakora kyauta, musamman a yankunan karkara da ba su da asibitocin hakori.

Nura Aliyu Sa’id, ya ce, kashi 80 cikin 100 na jama’a na fama da matsalar hakora , kuma shirin ya taimaka wajen gano cututtukan baki da suka dade suna boye a cikin yara, ciki har da wadanda suke yaduwa daga uwa zuwa jaririnta.

Ya kara da cewa, zamani ya wuce na cire hakori domin yanzu masana na da hanyoyin magance kowace irin matsalar hakori.

A nasa jawabin, Mataimakin shugaban shirin Mai Kula da shiyyar Rano, ‘Therapist’ Kabiru Ibrahim Dawakin Kudu, ya ce lalacewar hakori da sauran cututtukan baki na faruwa ne a saboda rashin tsafta da rashin wanke baki akai-akai.

Ya bukaci jama’a su rika wanke baki akai-akai, tare da neman shawarar kwarru akan man goge baki da burushin da ya dace da su.

Masana sun jaddada bukatar jama’a su rika zuwa asibiti domin duba hakoransu aƙalla sau biyu a shekara domin dubawa, da kuma neman magani da zarar sun ga canji a hakoransu.

Daga bisani, sun yaba da kokarin Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa daukar nauyin shirin, tare da jinjinawa sauran shugabanni da jama’a masu kishin al’umma da ke tallafawa wajen magance matsalolin lafiyar baki a jihar Kano.

Share188Tweet118SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Amurka Ta Amince da Yarjejeniyar Makamashin Nukiliya na Farar Hula da Saudiyya

Next Post

Gwamnan kano ya karbi lambobin girmamawa daban daban

Khadija Maitaya

Khadija Maitaya

RelatedPosts

Cutar mashako
LAFIYA

Cutar mashako

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Governor Yusuf commissions Kano center for disease control
LAFIYA

Governor Yusuf commissions Kano center for disease control

by Khadija Maitaya
August 4, 2026
An Kama Wata Matashiya Mai Shekaru 27 Bisa Zargin Satar Jariri A Asibiti A Zamfara
LAFIYA

An Kama Wata Matashiya Mai Shekaru 27 Bisa Zargin Satar Jariri A Asibiti A Zamfara

by aksam
May 17, 2026
Najeriya Sama Da 4,600 Ne Suka Koma Kasashen Waje Da Aiki A Cikin Shekaru 3 ‎ ‎—Rahoto
LAFIYA

Najeriya Sama Da 4,600 Ne Suka Koma Kasashen Waje Da Aiki A Cikin Shekaru 3 ‎ ‎—Rahoto

by aksam
April 22, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

INEC Ta Saka Ranakun Zaɓen 2027

INEC Ta Saka Ranakun Zaɓen 2027

February 13, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dage Aikin Tsaftar Muhalli na 26 ga watan Yuli

Gwamnnatin Kano ta kafa kwamatin Mutane bakwai domin gano gaskiyar karbar belin dilan kwaya da kwamishina yayi

July 26, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media