Daga: Hassan Umar Gwammaja
Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya na cigaba da tumbatsa da yin kane-kane a harkokin siyasar ƙasar.
Manya da ƙananan ƴan siyasa, daga gwamnoni zuwa sanatoci da ƴan majalisar tarayya da na jihohi na jam’iyyun adawa na ta tururuwar komawa cikin ta, lamarin da ya kai ga wasu ƴan siyasa ke fargabar cewa ƙasar na neman komawa tsarin jam’iyya ɗaya.
Sai dai wasu sun nuna cewa duk ƙarfin da APC take da shi a yanzu, a baya PDP ma ta samu irin shi, ta tumɓatsa kafin ta fara fashewa, har ta kai matsayin da take a yanzu na rashin tabbas.
Duk da cewa PDP ce ta zo ta biyu a babban zaɓen ƙasar na 2023, amma ya zuwa yanzu ta yi asarar wasu daga cikin jigoginta, kamar ɗan takararta na shugaban ƙasa Atiku Abubakar, da wanda ya mara masa baya a takarar, Ifeanyi Okowa, inda suka sauya sheƙa.











