Daga: Hassan Umar Gwammaja
Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya bayyana cewa matar marigayi tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, Hajiya Aisha Buhari, tana da matsayin uwa a gare shi da sauran mutanen da suka yi aiki a ƙarƙashin gwamnatin marigayin shugaban.
Pantami ya yi wannan bayani ne yayin da yake mayar da martani kan jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta wadda ke ikirarin cewa yana shirin auren Hajiya Aisha Buhari.
“Abin mamaki ne matuƙa yadda wasu ke ƙirƙirar irin wannan jita-jitar,” in ji Pantami.
“Marigayi Shugaba Buhari uba ne a gare mu, kuma matarsa uwa ce a wurinmu.”
“Wannan ikirari ba gaskiya ba ne, kuma abu ne da ba zai taɓa yiyuwa ba.”
Tsohon ministan ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da kafar yaɗa labarai ta PRNigeria.












