Yan bindiga sun tarwatsa mazauna kauyuka 10 musamman mata da ƙananan yara a yankin ƙaramar hukumar Giwa ta jihar Kaduna
An bayyana cewa galibin mazauna kauyukan sun zama ƴan gudun hijira a garin Giwa saboda yawaitar hare-haren ta’addanci a yankunansu
Gwamnatin Kaduna ta bayyana cewa ta fara ɗaukar matakan shawo kan lamarin da ƙara matakan tsaro a garuruwan da lamarin ya shafa
Ya ce mutane sun fara gudun hijira daga kauyukansu ne bayan hukumomi sun ɗauke wani jajirtaccen soja mai kwazo,
Sajan Usman Hamisu Bagobiri. A cewarsa, wannan soja na taka muhimmuyar rawa wajen yaƙar ƴan bindigar da suka addabi yankin, amma kwatsam aka canza masa wurin aiki. Ya ce tafiyar
Sajan Bagobori ya ƙarawa ƴan ta’addan kwarin guiwa, inda suka ci gaba da kai munanan hare-haren ta’addanci, wanda ya tilastawa mutane yin gudun hijira.
Bijimi ya ce kauyukan da lamarin ya shafa sun hada da Gogi, Angwar Bako, Marge, Tunburku, Bataro, Kayawa da Yuna, jaridar Punch ta ruwaito.
Ya kuma yi kira ga gwamnatin jihar da hukumomin soji da su mayar da Sajan Bagobiri bakin aiki tare da tura karin sojoji jajirtattu domin ci gaba da yaki da ‘yan bindigar.










