• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Majalisar ministocin Burkina Faso ta tsawaita waadin mulkin Soji a kasar

aksam by aksam
May 25, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Taron kasa ya tsawaita wa’adin mulkin soja na shekaru biyar a Burkina Faso

Shugaban mulkin Soji na Burkina Faso Kyaftin Ibrahim Traoré, wanda ya hau karagar mulki a watan Satumbar 2022 ta hanyar juyin mulki, zai tsawaita wa’adin mulkinsa na karin shekaru biyar, a cewar wata yarjejeniya da mahalarta taron kasa suka amince da ita a yau Asabar a babbann birnin kasar Ouagadougou.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

“An saita tsawon lokacin mika mulki a watanni 60 daga ranar 2 ga watan gobe,wato Yuli shekarar 2024,” in ji Kanar Moussa Diallo, shugaban kwamitin shirya wadannan tarurrukan.

Shugaba Traoré kuma zai iya kasancewa dan takara a zabukan kasar musaman neman kujearar shugaban kasa, ‘yan majalisa da na kananan hukumomi wadanda za a shirya don kawo karshen mika mulki”, in ji Kanar Diallo.

Taron ministocin kasashen yankin Sahel

Taron na kasa da aka shirya kammala shi a ranar Lahadin da ta gabata, ya hada wakilan kungiyoyin farar hula da na tsaro da na tsaro da ma wakilai daga majalisar rikon kwarya a ranar Asabar. Mafi akasarin jam’iyyun siyasa sun kauracewa taron.

A cikin sabuwar yarjejeniyar da Kyaftin Traoré ya rattabawa hannu a yau Asabar, an cire kujeru da aka saba warewa jam’iyyun siyasa wanda ya shafi  mukaman wakilai na majalisar rikon kwarya.

Burkina Faso, wacce ke fama da tashe tashen hankulan masu da’awar jihadi wadanda suka yi sanadin mutuwar dubban mutane kusan shekaru goma, ta fuskanci juyin mulkin soji guda biyu a shekarar 2022.

A cikin wannan tsari, an amince da wata yarjejeniya a tarurrukan kasa na farko, na samar da shugaban kasa, majalisar ministoci karkashin gwamnati, majalisar dokokin rikon kwarya (ALT) da kuma sanya lokacin mika mulki na watanni 21.

Don haka ya kamata a kawo karshen wannan mika mulki a ranar 1 ga Yuli, 2024, amma a lokuta da dama Kyaftin Traoré ya yi magana game da wahalar gudanar da zabe duba da yanayin tsaro a kasar ta Burkina Faso.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Rasha ta soma gina tashar wutar lantarki ta Sola mafi girma a Africa

Next Post

Wasu kasashen Europe uku sun amince da kasar Palastinu

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Ghana ta bude katafariyar matatar man fetur da China ta gina a kasar ta

Ghana ta bude katafariyar matatar man fetur da China ta gina a kasar ta

January 27, 2024

Kasar China ta bullo da sabbin tsare-tsare na tarbar baki

January 12, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media