Taron kasa ya tsawaita wa’adin mulkin soja na shekaru biyar a Burkina Faso
Shugaban mulkin Soji na Burkina Faso Kyaftin Ibrahim Traoré, wanda ya hau karagar mulki a watan Satumbar 2022 ta hanyar juyin mulki, zai tsawaita wa’adin mulkinsa na karin shekaru biyar, a cewar wata yarjejeniya da mahalarta taron kasa suka amince da ita a yau Asabar a babbann birnin kasar Ouagadougou.
“An saita tsawon lokacin mika mulki a watanni 60 daga ranar 2 ga watan gobe,wato Yuli shekarar 2024,” in ji Kanar Moussa Diallo, shugaban kwamitin shirya wadannan tarurrukan.
Shugaba Traoré kuma zai iya kasancewa dan takara a zabukan kasar musaman neman kujearar shugaban kasa, ‘yan majalisa da na kananan hukumomi wadanda za a shirya don kawo karshen mika mulki”, in ji Kanar Diallo.
Taron ministocin kasashen yankin Sahel
Taron na kasa da aka shirya kammala shi a ranar Lahadin da ta gabata, ya hada wakilan kungiyoyin farar hula da na tsaro da na tsaro da ma wakilai daga majalisar rikon kwarya a ranar Asabar. Mafi akasarin jam’iyyun siyasa sun kauracewa taron.
A cikin sabuwar yarjejeniyar da Kyaftin Traoré ya rattabawa hannu a yau Asabar, an cire kujeru da aka saba warewa jam’iyyun siyasa wanda ya shafi mukaman wakilai na majalisar rikon kwarya.
Burkina Faso, wacce ke fama da tashe tashen hankulan masu da’awar jihadi wadanda suka yi sanadin mutuwar dubban mutane kusan shekaru goma, ta fuskanci juyin mulkin soji guda biyu a shekarar 2022.
A cikin wannan tsari, an amince da wata yarjejeniya a tarurrukan kasa na farko, na samar da shugaban kasa, majalisar ministoci karkashin gwamnati, majalisar dokokin rikon kwarya (ALT) da kuma sanya lokacin mika mulki na watanni 21.
Don haka ya kamata a kawo karshen wannan mika mulki a ranar 1 ga Yuli, 2024, amma a lokuta da dama Kyaftin Traoré ya yi magana game da wahalar gudanar da zabe duba da yanayin tsaro a kasar ta Burkina Faso.











