Daga: Hassan Umar Gwammaja
A ranar Asabar dinnan 12 ga watan Zulhijja,1446AH wace ta yi daidai da 8 ga watan June, 2025 Mai Martaba Sarkin Jama’a Alhaji Dakta Muhammad Isa Muhammed Na ll OFR, CON, ya gudanar da Hawan Daushe a Garin Kafanchan Dake Jihar Kaduna
Tun da farko Sarkin ya fitone daga Gidansa zuwa Babban Asibitin Tunawa da Sir Patrick Ibrahim Yakowa daga cikin garin Kafanchan domin kai ziyara da bada kyauttutukan magunguna ga masa lafiya
In da ya samu taran Hakimai da Dakatai da wakilin Gwamnatin Jihar Kaduna Sanata Uba Sani, Wanda Kwamishinan Jinkai Da Walwallar Jama’a Comred Markus Yunana Barda ya wakilceshi da kuma dinbin al’ummar Garin Kafanchan, harma Sarkin ya bayyana wasu bukatunsu ga Gwamnatin Jihar Kaduna na ganin an bar Asibitin da Gwamnatin Kaduna ta gina a garin Kafanchan domin sauwakawa marasa lafiya










