Kungiyar yan kasuwar Man Fetur ta Najeriya sun bayyana cewa Shugaban rukunin Kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Ɗangote shine ne ya haifar da matsala da Ma’aikatan da ke a ɓangaren Man Fetur da iskar Gas waɗanda su ne za su taimaka burin Matatar Man tasa na tace ganga 650,000 a kowace rana yayi nasara.
Shugaban Ƙungiyar ƴan kasuwar Man Fetur ta Najeriya Billy Gillis Harry ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa ta Musamman da ya yi da jaridar Dimokuraɗiyya.
Ya yi magana ne a kan takaddamar da ke tsakanin Matatar Man Dangote da Hukumar Kula da Man Fetur ta Najeriya NUPRC kan batun samar da gangar danyen Mai Miliyan 26.
Da yake tsokaci dangane da lamarin Gillis Harry ya bayyana cewa ba zai yiwu ba matatar mai da ke Legas ta Ɗangote ta fara aikin tace mai ba tare da samun isassun danyen Man ba.
A cewarsa Matatar man Dangote kadai ba za ta iya karbar gangar danyen Mai Miliyan 26 ba muddin akwai wasu Matatun Mai na cikin gida a Najeriya.
Ya ce kamata ya yi dukkan masu ruwa da tsaki su yi taron tattaunawa don warware rikicin da ake fama da shi a harkar Mai da iskar gas a Kasar.
Yace Ɗangoten ne ya haifar da cece-kuce tsakaninsa da waɗanda ya kamata su taimaka masa wajen magance ƙalubalen samar da danyen Mai.
Idan sun kasa magance matsalar danyen Mai, ban ga ta yadda zai fara tace Man Fetur ba.
Ɗangote yana yaudarar kansa ne kawai, Babu yadda za a yi a baiwa Matatarsa ganga Miliyan 26 shi kaɗai ba alhalin ma ba ya da cikakken lasisi.
Dukkanin waɗanda abin ya shafa dole ne su zauna su yi nazarin hanyoyin magance matsalolin.












