Mali, Nijar, da Burkina Faso, bayan ficewarsu daga kungiyar ECOWAS, sun shiga kawancen kasashen Sahel ta AES, yanzu haka sun sanya harajin kwastam na kashi 0.5 cikin 100 na kayayyakin da ake shigowa da su daga kasashen da ba su cikin wannan kungiya ta AES.
A cikin watan Janairu ne ƙasashen Sahel uku suka fice daga kungiyar ECOWAS wacce suke ganin ta kasance karkashin kasashen mulkin mallaka, inda suka kafa kawancen kasashen Sahel (AES).
Sai dai har yanzu suna cin moriyar kungiyar da suka hada da zirga-zirgar jama’a da kayayyaki, har sai an cimma yarjejeniya tsakanin bangarorin biyu kan sharudan rabuwar da ya kamata a yi nan ba da dadewa ba.
A halin da ake ciki, kasashen uku sun kafa wani shiri na hadin gwiwa na “AES kan kasashen da ba mambobin kungiyarsu da kuma wadanda ba su da yarjejeniyar kwastam da su, kamar yadda wata takardar da shugaban mulkin sojan Mali kuma shugaban kungiyar AES, Janar Assimi Goïta ya sanya wa hannu.
Za a yi amfani da albarkatun da aka samar don samar da kuɗi, musamman, ayyukan taimakawa wannan kungiya ta AES, gina ƙasashen,samarwa jama’a kayakin more rayuwa da dai sauren su.
Kayayyakin da ke wucewa, taimako, gudummawa da tallafin da ba za a iya mayarwa ba ,dokar ta kwastam ba ta shafe su ba.
A cewar Ministan Tattalin Arziki da Kuɗi na Mali Alousséni Sanou, wannan harajin “ba wani ƙarin nauyi ba ne.”
“Muna da harajin ECOWAS na al’umma wanda ya kasance daidai gwargwado kuma an yi amfani da shi akan tsari guda,” in ji shi a gidan talabijin na kasar.












