DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Wani karamin jirgin saman rundunar sojan saman Najeriya ya yi hatsari da safiyar ranar Litinin ne a kauyen Tami dake karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.
Shaidar gani da ido ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 5 na safe abinda ya haifar da firgici ga al’ummar yankin.
Rahotanni sun bayyana cewa jirgin na kan hanyar sa ta aiki yayin da ya fuskanci matsala wacce ta kai ga faduwarsa.
Sai dai bayanai sun nuna cewa matukin jirgin ya samu tsira.










