Da fari dai, asalin wannan fitina ta fito ne daga Amurka, kuma hakan a bayyane yake. Amurkawa ne suka tsara ta kuma suka aiwatar da ita.
• Manufar Amurka — kuma ina faɗin wannan a sarari kuma a bayyane bisa gogewa sama da shekaru 40 a Jamhuriyar Musulunci — ita ce cinye Iran.
• Tun daga farkon Juyin Juya Halin Musulunci zuwa yau, irin ikon da suke da shi a kan wannan ƙasa ya rushe sakamakon tashi tsaye na jama’a, matasa, da dukkanin al’ummar ƙasar, ƙarƙashin jagorancin Babban Imam.
• Tun daga rana ta farko, suna tunanin dawo da wannan iko, wato mayar da Iran ƙarƙashin ikon su na soja, siyasa da tattalin arziƙi.
• Wannan ita ce manufar. Ba batun shugaban Amurka na yanzu ba ne, ko wanda ya bar mulki; magana ce game da manufar Amurka gaba ɗaya.
• Manufar Amurka ita ce: ƙasa mai irin waɗannan siffofi, a irin wannan muhimmin matsayi na ƙasa, mai irin waɗannan ƙwarewa, girma da yawan jama’a… ba za su iya jurewa ba.
• Ƙasa irin wannan, wadda ke samun ci gaba a fannonin kimiyya da fasaha daban-daban, abin ƙi ne a wurin Amurkawa.
• Muna ɗaukar shugaban Amurka a matsayin mai aikata laifi, saboda asarar rayuka, barnar da aka yi, da kuma ƙazafin da ya yi wa al’ummar Iran.
• A baya, idan irin wannan tarzoma ta faru, yawanci ‘yan jarida na Amurka, ‘yan siyasa na mataki na biyu, ko ƙasashen Turai ne ke shiga tsakani.
• Abin da ya bambanta wannan tarzoma shi ne, shugaban Amurka da kansa — kai tsaye — ya shiga tayar da fitina da kuma ƙarfafa ta.
• Ya yi magana, ya yi tsokaci, ya yi barazana, ya ƙarfafa masu tayar da hankali, ya kuma aika saƙonni daga Amurka zuwa gare su, yana cewa kada su ji tsoro, yana cewa “muna tare da ku; za mu ba ku tallafin soja.” Wato shugaban Amurka da kansa ya shiga cikin wannan fitina.
• Wasu daga cikin masu tayar da hankalin, waɗanda suka aikata lalata, ƙone-ƙone, ayyukan ba bisa ƙa’ida ba da kisan kai, ya gabatar da su a matsayin al’ummar Iran.
• Wannan babbar ƙazafi ce ga al’ummar Iran. Ya ce, “Waɗannan su ne al’ummar Iran; ina so in kare al’ummar Iran.” Waɗannan laifuka ne.
• Dalilan da na ambata hujjoji ne da aka rubuta; babu abin ɓoye. Ya yi magana a fili, ya ƙarfafa a fili. Muna da shaidu na ci gaba cewa sun ba da taimako, su da kuma gwamnatin sahyoniya, wanda zan ambata a taƙaice daga baya.
• Hakika, al’ummar Iran sun karya kashin bayan fitinar.
• Al’ummar Iran, da miliyoyin mutane a Tehran da kuma manyan taruka a sauran birane da dama, sun iya kai mummunan martani ga masu ikirarin ƙarya. Godiya ta tabbata ga Allah.
• Al’ummar Iran sun kayar da Amurka. Amurkawa sun ƙaddamar da wannan fitina da manyan shirye-shirye domin cimma manyan manufofi. Al’ummar Iran sun ci galaba a kanta.
• Wannan gaskiya ne, amma bai wadatar ba. Mun kashe wutar fitinar, amma hakan bai isa ba. Dole ne a ɗauki Amurka da alhaki.
• Ba mu tura ƙasar zuwa yaƙi ba, kuma ba mu da niyyar tura ƙasar zuwa yaƙi. Amma ba za mu yi watsi da masu aikata laifi a cikin gida ba.
• Mafi muni fiye da masu aikata laifi a cikin gida su ne masu aikata laifi na ƙasa da ƙasa; su ma ba za mu barsu ba. Dole ne a bi wannan lamari ta hanyoyin da suka dace.
• Kuma da ikon Allah, kamar yadda al’ummar Iran suka karya kashin bayan fitinar, dole ne su kuma karya kashin bayan masu tayar da fitina.











