Daga: Hassan Umar Gwammaja
In da ta kasu gida uku sakamakon takaddama kan jagorancin jam’iyyar.
Rikicin ya haɗa da ɓangarori ƙarƙashin jagorancin Babachir Devic Lawal, Dana Aishatu Ahmed, Da Kuma Ishaku Abbo
Sai dai ɓangarorin Sanata Binani da Abbo sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar, suna zargin rushewar dimokuraɗiyya da kuma maguɗin zaɓe wajen nadin shugabanni.
Abbo ya ce zai sanar da sabuwar jam’iyyar da zai koma nan ba da jimawa ba, yana mai kira ga magoya bayansa su shirya tunkarar zaɓen 2027.
Lamarin ya jefa ADC cikin babban gibi a jihar, tare da ƙara nuna tsanantar rikicin cikin gida gabanin zaɓen 2027 mai zuwa.












