Shugabancin Jam’iyyar PDP na Kano, tsagin Ibrahim Al’Amin Little da kuma Honarabul Sadiq Aminu Wali, ya yi zargin tsohon gwamnan Kano, Sanata Malam Ibrahim Shekarau da raba Jam’iyyar gida biyu.
Little, ya bayyana zargin ne yayin taron manema Labarai, jim kadan da kammala wani taron Shugabannin Jam’iyyar na kananan hukumomi 44, domin dawo da martabar Jam’iyyar a lungu da sako na jihar Kano.
Little ya kara da cewa, Tsagin Shekarau sun raba Jam’iyyar gida biyu ne a sakamakon yadda suka haddasa rikicin cikin gida a tsakanin ‘ya ‘yan Jam’iyyar.
“Wannan dalili ne ya sanya shugabancin tsagin namu ya dauki dukkan matakan da suka kamata, domin farfado da farin jinin Jam’iyyar a fagen siyasar jihar Kano”.
Bugu da kari ya ce sun himmatu wajen hada hannu da dukkan masu ruwa da tsakin Jam’iyyar na matakin kananan hukumomi da kuma Mazabu, domin dinke barakar Jam’iyyar tun daga tushe ta yadda zasu cimma nasarar da ake bukata.
Manufar Tsagin Little da Wali shine farfado da martabar Jam’iyyar a jihar Kano, dama ci-gaba da rike Kambunta domin ta sami damar yin nasara a kakar zaben dake tafe.











