A ranar Litinin 18 ga watan Agusta ne hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta fara aikin rajistar masu zaɓe a faɗin ƙasar, ta hanyar intanet gabanin fara aikin a ofisoshinta da ke faɗin ƙasar a mako mai zuwa.
INEC kan bai wa ƴan Najeriya damar yin rajistar zaɓe a duk lokacin da aka tunkari kakar babban zaɓe a ƙasar.
Dama ce da hukumar ke bai wa ƴan Najeriya da suka cika shekara 18, ko waɗanda wasu dalilai suka hana yin rajistar a shekarun baya ko kuma wani tsautsayi ya sa rijistar tasu ta ɓata.
Hukumar za ta ci gaba da aikin ne har zuwa dab da zaɓukan 2027, don haka ne ma take kiran aikin rajistar zaɓen da ”Ci Gaba da Rajistar Masu Zaɓe”, wato ”Continuous Voter Registration” a Turance (CVR).












