Hukumar Kula da Zirga-Zirgar Ababan Hawa ta Jihar Kano (KAROTA) ta kaddamar da kotunan tafi-da-gidanka domin gudanar da shari’ar gaggawa kan direbobi da ke karya dokar fitulun ba da hannu a manyan titunan birnin Kano.
Da yake kaddamar da kotunan, Shugaban Hukumar KAROTA, Faisal Mahmud Kabir, ya bayyana cewa wannan mataki ya biyo bayan umarnin da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bai wa hukumar domin tabbatar da cikkaken bin dokokin zirga-zirga daga direbobi da masu tukin adaidaita sahu.
Shugaban ya jaddada cewa ganin yadda gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta zuba makudan kudade wajen samar da sabbin fitilun hasken wuta masu amfani da rana haske rana, dole ne masu ababen hawa da masu adaidaita su nuna godiya ta hanyar bin dokokin fitulun ba da hannun.
Ya ja kunnen duk direban da aka kama yana karya dokar cewar jami’an KAROTA tare da hadin gwiwar jami’an tsaro za su cafke shi domin a gudanar da shari’a nan take a gaban kotun tafi-da-gidanka.
Faisal Mahmud Kabir ya kuma bukaci jama’a da su ba da hadin kai ga jami’an KAROTA, yana mai tabbatar da cewa kotunan ba don tsoratarwa ko cin zarafin wani ba ne, illa kawai don kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yayin da suke zirga-zirga a tituna.
Shugaban na KAROTA ya ce hukumar ba zata saurara ba kowa ba wajen aiwatar da manufofi da shirye-shiryen raya harkokin sufuri na Gwamnatin Kano wadanda suka mayar da hankali kan jin dadin al’umma.
Ta cikin wani jawabi da ya fitar Abubakar Ibrahim Sharada Jami’in Hulda da Jama’a, na hukumar KAROTA, ya tunatar tuni a baya Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) reshen Kano ta tabbatar da goyon bayan ta ga KAROTA wajen tabbatar da bin dokokin hasken wuta da kuma kama masu karya doka.












