Daga: Hassan Umar Gwammaja
Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce, sakamakon rikice-rikicen da ke addabar Jam’iyyar NNPP, tare da gazawar shawo kan matsalolin da suka taso, hakan ya tilasta musu ɗaukar wannan mataki.
Ya ƙara da cewa an ɗauki matakin ne da kyakkyawar niyya, domin la’akari da buƙatun al’ummar Jihar Kano da kuma cigaban jihar baki ɗaya.
Gwamnan ya ce tuni ya sanar da shugaban jam’iyyarsa na mazaɓarsa da ke Disu a Ƙaramar Hukumar Gwale game da ficewarsa daga jam’iyyar.
Ya bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne tare da shugabannin ƙananan hukumomi na Jihar Kano, da kuma wasu ‘yan Majalisun Tarayya da na Jiha.
A ƙarshe, Gwamnan ya gode wa Jam’iyyar NNPP bisa damar da ta ba shi, wanda hakan ya ba shi damar zama gwamnan Jihar Kano a ƙarƙashin tutar jam’iyyar.











