Lauyoyin Aminu Ado Bayero, sun fice daga shari’ar dambarwar masarautar Kano da ake yi a babbar kotun jihar Kano.
Lauyoyin sun ɗauki matakin ne a zaman kotun da ya gudana a ranar Alhamsi, bayan kai ruwa rana tsakanin ɓangarorin da ke shari’a da juna.
A zama kotun lauyan Aminu Ado Bayero, Abdul Muhammed, ya fara da shaida wa kotun cewa akwai takardar da ta ke tabbatar da cewa sun ɗaukaka ƙara kuma an shigar da bayanan a gaban kotun, kuma ya nemi kotun da kada ta ci gaba da sauraron shari’ar har sai an saurari ɗaukaka ƙarar da suka yi.
Lauyan ya kuma buƙaci kotun ta ƙara musu lokaci don mayar da martani kan wasu takardu da ya ce an ba su ranar Laraba.
To sai dai ɓangaren masu ƙara sun soki waɗannan buƙatu, inda babban lauyan gwamnatin Kano da majalisar dokokin jihar, Eyitayo Fatogun ya ce babu waɗannan bayanan a kotun.
Kana ya shaida wa kotun cewa ba haka ake yi ba, yana mai cewa dokokin babbar kotu sun ce idan kana so ka shigar da wasu bayanai a gaban kotu nema ake yi ba kawai ka kawo wata takarda ba.
Bayan sauraron duka ɓangarorin biyu, Mai shari’a Amina Adamu Aliyu ta ce buƙatun da lauyan Aminu Ado Bayero ya gabatar ba su da karfin da za su hana ci gaba da sauraron shari’ar don haka ta yi watsi da su.
Inda ta bayar da umarnin ci gaba da sauraron shari’ar da ke gaban kotun
To sai dai wannan hukunci bai yi wa lauyoyin Aminu Ado Bayero daɗi ba, inda Barrister Sanusi Musa ya mike ya shaida wa kotun cewa sun fice daga wannan shari’a, sannan ya ce za su koma su sanar da wanda suke wakilta don ya nemi wanda zai wakilce shi, sannan suka fice daga kotun.











