• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Dambarwar masarautu: bayan saka ranar yanke hukunci layan wani bangare ya aje aikin kare wanda yake wakilta

aksam by aksam
July 5, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Lauyoyin Aminu Ado Bayero, sun fice daga shari’ar dambarwar masarautar Kano da ake yi a babbar kotun jihar Kano.

Lauyoyin sun ɗauki matakin ne a zaman kotun da ya gudana a ranar Alhamsi, bayan kai ruwa rana tsakanin ɓangarorin da ke shari’a da juna.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

 A zama kotun lauyan Aminu Ado Bayero, Abdul Muhammed, ya fara da shaida wa kotun cewa akwai takardar da ta ke tabbatar da cewa sun ɗaukaka ƙara kuma an shigar da bayanan a gaban kotun, kuma ya nemi kotun da kada ta ci gaba da sauraron shari’ar har sai an saurari ɗaukaka ƙarar da suka yi.

Lauyan ya kuma buƙaci kotun ta ƙara musu lokaci don mayar da martani kan wasu takardu da ya ce an ba su ranar Laraba.

To sai dai ɓangaren masu ƙara sun soki waɗannan buƙatu, inda babban lauyan gwamnatin Kano da majalisar dokokin jihar, Eyitayo Fatogun ya ce babu waɗannan bayanan a kotun.

 Kana ya shaida wa kotun cewa ba haka ake yi ba, yana mai cewa dokokin babbar kotu sun ce idan kana so ka shigar da wasu bayanai a gaban kotu nema ake yi ba kawai ka kawo wata takarda ba.

Bayan sauraron duka ɓangarorin biyu, Mai shari’a Amina Adamu Aliyu ta ce buƙatun da lauyan Aminu Ado Bayero ya gabatar ba su da karfin da za su hana ci gaba da sauraron shari’ar don haka ta yi watsi da su.

Inda ta bayar da umarnin ci gaba da sauraron shari’ar da ke gaban kotun

To sai dai wannan hukunci bai yi wa lauyoyin Aminu Ado Bayero daɗi ba, inda Barrister Sanusi Musa ya mike ya shaida wa kotun cewa sun fice daga wannan shari’a, sannan ya ce za su koma su sanar da wanda suke wakilta don ya nemi wanda zai wakilce shi, sannan suka fice daga kotun.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Abin da yakamata ku sani Akan yarjejeniyar bada Kariya ga masu auren Jin da Najeriya ta saka hanu

Next Post

Ana Fargabar Samun Karancin Man Fetur A Najeriya

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Yadda Yan kasuwar kayayyakin gona ke kokawa da farashin man fetur

Yadda Yan kasuwar kayayyakin gona ke kokawa da farashin man fetur

September 28, 2023

Top Strategies for Winning at Casino War at casigood casino

April 21, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media