Dan ta’adda da ya yi kaurin suna a Arewa maso yammacin Najeriya wato Bello Turji ya amince da tayin al’ummar garin Moriki ta jihar Zamfara su biya naira miliyan 30 maimakon miliyan 50 da ya bukuta, a baya a matsayin kudin diyya kwashe amfanin gonakinsu.
Turji ya tilas ta wa al’ummar garin su biya wadannan makudan kudin zuwa ranar Laraba, biyo bayan kashe mashi shanu da Sabon kwamandan Sojoji yankin yayi.
Audu Bulama Bukarti ya wallafa a shafin sa cewa, An bukaci ko wani magidanci da ya bayar da naira dubu 10, yayin da wadanda basu da aure zasu biya naira dubu 2 duk kuwa da yunkurin hana bada wadannan kudaden da kwamandan Sojojin yayi.












