• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Baya ga kayan abinci, kasar Russia ta aike da tallafin motoci makare da makamai ga kasar Niger

aksam by aksam
April 13, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Gwamnatin rikon kwaryar jamhuriyar Nijar ta sanar da isowar wasu makamai da na’urorin kare sararin samaniyar da tace sun shigo ne albarkacin huldar ayyukan sojan dake tsakanin Nijar din da Russia.

Tashar talbijan RTN mallakar gwamnati ta gwada wani jirgin da ta ayyana a matsayin wanda ke dauke da lodin makaman da suka iso birnin Yamai tare da sojojin Rasha kimanin 100 da za su yi aikin girka wadanan makamai su kuma bai wa takwarorinsu na kasar horo akan yadda za su yi amfani da su.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Jirgin dakon kaya samfarin ILYUSHIN 76 ne ya sauka filin jirgin saman Yamai a cikin daren Laraba zuwa wayewar Alhamis dauke da makaman kare kai daga hare-haren sama hade da wasu na’urorin kariyar sararin samaniya kamar yadda ake gani a wani rahoton da gidan talbijan mallakar gwamnatin Nijar ya watsa.

Wannan wani bangare ne na sabuwar huldar da hukumomin mulkin soja suka kulla da gwamnatin Vladimir Putin a ci gaba da laluben hanyoyin magance matsalolin tsaron da kasar ke fuskanta. Masani a kan lamuran yankin sahel Dr. Seidik Abba na cewa bai yi mamakin wannan yunkuri na Rasha ba.

Wasu sojojin gwamnatin Rashar a kalla 100 ne aka bayyana cewa sun biyo wadanan kayayyaki da za su jagoranci ayyukan girkawa sannan zasu horar da takwarorinsu na kasar a game da yadda zasu yi amfani da su kamar yadda wani kakakin tawwagar rashawan ya jaddada.

Jigo a kungiyar Front Patriotique ta ‘yan goyon bayan hukumomin CNSP Bana Ibrahim na mai alfahari da abinda ya kira sabuwar tafiya.

Sai dai wani dan fafutika Amadou Roufai Laouan Salao na gamayyar COADDE na da shakku kan tasirin wannan hulda tsakanin Rasha da Nijar.

Ayyukan ashan da ake zargin sojan hayar Rasha a kasashen da kamfanin Wagner ke da kwangila abu ne da ya kamata ya zame wa Nijar manuniya inji Souley Oumarou shugaban kungiyar FCR.

Gwamnatin rikon kwaryar Jamhuriyar Nijar ta sanar da isowar wasu makamai da tace sun shigo ne albarkacin huldar tsakanin kasar da Russia.

Gwamnatin rikon kwaryar Jamhuriyar Nijar ta sanar da isowar wasu makamai da tace sun shigo ne albarkacin huldar tsakanin kasar da Russia.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Yi Alkawarin Ci Gaba Da Ciyar Da Daliban Makarantun Firamaren Jihar

Next Post

Yadda kananan masana’antu ke koka wa da karin kudin wutar lantarki

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Shawarwarin masana ga Dalibai masu neman ilimi

Shawarwarin masana ga Dalibai masu neman ilimi

October 22, 2023
Ministan Kuɗi Kuma Ministan Haɗa-hadar Tattalin Arziki na Najeriya, Wale Edun, Ya Yi Kira Da a Sake Fasalta Tsarin Tattalin Arzikin Duniya Gaba Daya

Ministan Kuɗi Kuma Ministan Haɗa-hadar Tattalin Arziki na Najeriya, Wale Edun, Ya Yi Kira Da a Sake Fasalta Tsarin Tattalin Arzikin Duniya Gaba Daya

February 9, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media