• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda kananan masana’antu ke koka wa da karin kudin wutar lantarki

aksam by aksam
April 13, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
469
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga I S Gama

Kungiyar masu Kananan Masana’antu ta jihar Kano, ta bi sahun Kungiyoyin Masana’antu na Kasa dangane da Kokawa akan Karin kudin wutar lantarki da Gwamnatin tarayya ta yi da cire tallafi a harkokin Samar da wutar lantarkin Kasar nan.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Sakataren Kungiyar na jihar Kano,Ibrahim Bashir Nasambo ne ya bayyana haka a lokacin da yake ganawa da Manema labarai a ofishinsa dake rukunin Kamfanonin na Sharada a nan Kano.

Ibrahim Bashir Nasambo yace,cire tallafin wutar da Gwamnatin tarayya ta yi yana Neman kassara Masana’antu ya mayar da su kamar kufai,Wanda hakan zai janyo rashin ayyukan yi da kara karyewar tattalin Arzikin Kasa.

Sakataren ya bukaci Gwamnatin tarayya da sauran masu Ruwa da tsaki a fannin harkokin Samar da wutar lantarki,da su kawowa bangaren daukin gaggawa.

Yace,idon za’a iya tunawa haka aka yi bangaren cire tallafin man fetur da Gwamnatin tarayya ta yi, Wanda aka rika tunanin cewa,wasu ‘yan tsirarun mutane ne ke amfana da tallafin man, Amma sai gashi komai ya koma kan Talakawa.

Bashir Nasambo ya kara da cewa,Akwai bukatar Gwamnatin tarayya ta sake dogon Nazari da tunani mai zurfi wajen ganin ta kara rage Kudaden da masu Masana’antu suke biya domin basu wutar lantarki.

Ibrahim Bashir Nasambo ya Shawarci ‘ya’yan Kungiyar da su sauya sabon tsari wajen yadda za su gudanar da ayyukansu na harkokin Masana’antu domin aiwatar da Sana’arsu yadda ta kamata.

Yace, wannan yanayi da ake ciki na kara tsadar kudin wutar lantarki da cire tallafin wutar lantarkin zai haifar da matsaloli da yawa a fannoni da dama na Kasuwanci da tashin farashin kayayyakin Masarufi a Kasuwanni.

Haka Zalika,yace,Kungiyar Masu Kananan Masana’antu ta jihar Kano a shirye take wajen baiwa Gwamnatoci hadin kai a matakai daban daban domin kara bunkasa tattalin arzikin Kasar nan.

Sakataren ya kuma Shawarci ‘ya’yan Kungiyar da su kara jajircewa wajen baiwa Kungiyar cikakken hadin kan daya kamata domin ta samu damar kare hakkokin ‘ya’yanta da Samar musu da ci gaba a Kungiyar.

Ibrahim sani gama pyramid radio.

Share188Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Baya ga kayan abinci, kasar Russia ta aike da tallafin motoci makare da makamai ga kasar Niger

Next Post

Yadda Israel ke fuskantar muggan hare-hare daga kasar Iran

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Da DUMI-DUMI: Rundunar Yan sanda ta shirya samar da tsaro ga masu gudanar da zanga-zanga na tsawon kwanaki 10

Yanzu-yanzu I G na kasa ya bada umarni mai tsauri kan masu zanga-zangar kuncin rayuwa

August 1, 2024

How to Maximize Your Winning Potential at 666 casino

April 21, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media