Daga I S Gama
Kungiyar masu Kananan Masana’antu ta jihar Kano, ta bi sahun Kungiyoyin Masana’antu na Kasa dangane da Kokawa akan Karin kudin wutar lantarki da Gwamnatin tarayya ta yi da cire tallafi a harkokin Samar da wutar lantarkin Kasar nan.
Sakataren Kungiyar na jihar Kano,Ibrahim Bashir Nasambo ne ya bayyana haka a lokacin da yake ganawa da Manema labarai a ofishinsa dake rukunin Kamfanonin na Sharada a nan Kano.
Ibrahim Bashir Nasambo yace,cire tallafin wutar da Gwamnatin tarayya ta yi yana Neman kassara Masana’antu ya mayar da su kamar kufai,Wanda hakan zai janyo rashin ayyukan yi da kara karyewar tattalin Arzikin Kasa.
Sakataren ya bukaci Gwamnatin tarayya da sauran masu Ruwa da tsaki a fannin harkokin Samar da wutar lantarki,da su kawowa bangaren daukin gaggawa.
Yace,idon za’a iya tunawa haka aka yi bangaren cire tallafin man fetur da Gwamnatin tarayya ta yi, Wanda aka rika tunanin cewa,wasu ‘yan tsirarun mutane ne ke amfana da tallafin man, Amma sai gashi komai ya koma kan Talakawa.
Bashir Nasambo ya kara da cewa,Akwai bukatar Gwamnatin tarayya ta sake dogon Nazari da tunani mai zurfi wajen ganin ta kara rage Kudaden da masu Masana’antu suke biya domin basu wutar lantarki.
Ibrahim Bashir Nasambo ya Shawarci ‘ya’yan Kungiyar da su sauya sabon tsari wajen yadda za su gudanar da ayyukansu na harkokin Masana’antu domin aiwatar da Sana’arsu yadda ta kamata.
Yace, wannan yanayi da ake ciki na kara tsadar kudin wutar lantarki da cire tallafin wutar lantarkin zai haifar da matsaloli da yawa a fannoni da dama na Kasuwanci da tashin farashin kayayyakin Masarufi a Kasuwanni.
Haka Zalika,yace,Kungiyar Masu Kananan Masana’antu ta jihar Kano a shirye take wajen baiwa Gwamnatoci hadin kai a matakai daban daban domin kara bunkasa tattalin arzikin Kasar nan.
Sakataren ya kuma Shawarci ‘ya’yan Kungiyar da su kara jajircewa wajen baiwa Kungiyar cikakken hadin kan daya kamata domin ta samu damar kare hakkokin ‘ya’yanta da Samar musu da ci gaba a Kungiyar.
Ibrahim sani gama pyramid radio.











