• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda kananan masana’antu ke koka wa da karin kudin wutar lantarki

aksam by aksam
April 13, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
469
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga I S Gama

Kungiyar masu Kananan Masana’antu ta jihar Kano, ta bi sahun Kungiyoyin Masana’antu na Kasa dangane da Kokawa akan Karin kudin wutar lantarki da Gwamnatin tarayya ta yi da cire tallafi a harkokin Samar da wutar lantarkin Kasar nan.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Sakataren Kungiyar na jihar Kano,Ibrahim Bashir Nasambo ne ya bayyana haka a lokacin da yake ganawa da Manema labarai a ofishinsa dake rukunin Kamfanonin na Sharada a nan Kano.

Ibrahim Bashir Nasambo yace,cire tallafin wutar da Gwamnatin tarayya ta yi yana Neman kassara Masana’antu ya mayar da su kamar kufai,Wanda hakan zai janyo rashin ayyukan yi da kara karyewar tattalin Arzikin Kasa.

Sakataren ya bukaci Gwamnatin tarayya da sauran masu Ruwa da tsaki a fannin harkokin Samar da wutar lantarki,da su kawowa bangaren daukin gaggawa.

Yace,idon za’a iya tunawa haka aka yi bangaren cire tallafin man fetur da Gwamnatin tarayya ta yi, Wanda aka rika tunanin cewa,wasu ‘yan tsirarun mutane ne ke amfana da tallafin man, Amma sai gashi komai ya koma kan Talakawa.

Bashir Nasambo ya kara da cewa,Akwai bukatar Gwamnatin tarayya ta sake dogon Nazari da tunani mai zurfi wajen ganin ta kara rage Kudaden da masu Masana’antu suke biya domin basu wutar lantarki.

Ibrahim Bashir Nasambo ya Shawarci ‘ya’yan Kungiyar da su sauya sabon tsari wajen yadda za su gudanar da ayyukansu na harkokin Masana’antu domin aiwatar da Sana’arsu yadda ta kamata.

Yace, wannan yanayi da ake ciki na kara tsadar kudin wutar lantarki da cire tallafin wutar lantarkin zai haifar da matsaloli da yawa a fannoni da dama na Kasuwanci da tashin farashin kayayyakin Masarufi a Kasuwanni.

Haka Zalika,yace,Kungiyar Masu Kananan Masana’antu ta jihar Kano a shirye take wajen baiwa Gwamnatoci hadin kai a matakai daban daban domin kara bunkasa tattalin arzikin Kasar nan.

Sakataren ya kuma Shawarci ‘ya’yan Kungiyar da su kara jajircewa wajen baiwa Kungiyar cikakken hadin kan daya kamata domin ta samu damar kare hakkokin ‘ya’yanta da Samar musu da ci gaba a Kungiyar.

Ibrahim sani gama pyramid radio.

Share188Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Baya ga kayan abinci, kasar Russia ta aike da tallafin motoci makare da makamai ga kasar Niger

Next Post

Yadda Israel ke fuskantar muggan hare-hare daga kasar Iran

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Yanzu-yanzu, Isra’ila ta farmaki gidan talabijin na Iran ana tsaka da shirye-shirye

Yanzu-yanzu, Isra’ila ta farmaki gidan talabijin na Iran ana tsaka da shirye-shirye

June 16, 2025

Bayan yanke hukuncin kano Zamfara pilato bangaren sharia ya fara farfado da kimar sa: wani babban lauya

January 14, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media