DAGA:- HASSAN UMAR GWAMMAJA
Sakataren jam’iyyar APC na jiha Alhaji Zakari Sarina da mataimakin shugaban jam’iyyar NNPP ta Kudu, Alhaji Ibrahim Daho ne suka karyata rahotannin a wata ganawa da shugabannin hukumomin tsaro a hedikwatar rundunar ‘yan sandan jihar Kano.
Duk ya ce tuni bangarorin suka rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a kwanakin baya da nufin tabbatar da zaman lafiya kafin da kuma bayan hukuncin kotun daukaka kara, yana mai jaddada cewa, “mun tsaya kan maganarmu”.
Ba mu da wani tunanin wasu mutane na shirin gudanar da wata zanga-zanga, ba mambobinmu ba ne; mun umurci dukkan magoya bayanmu da su kasance masu bin doka da oda,” inji su.












