Daga Abdullahi Dan Bala Gwarzo
Yayin da watan Zul-Hijjah ke gabatowa, masana addinin Musulunci na kara jan hankalin al’umma game da falalar kwanaki goma na farko na wannan wata mai albarka, tare da ba da shawarwari kan yadda za a amfana da su cikin ibada da kyawawan ayyuka.
A wata tattaunawa da Aminiya, tsohon shugaban hukumar hisbah na jahar kano ,kuma shugaban makarantar koyar da aikin hajji da Umar, sheikh Haroon muhd sani ibn sina Kano, ya bayyana cewa wannan lokaci na daga cikin mafiya daraja a cikin dukkan watanni na shekarar.
Ya ce, “Wannan kwanaki ne mafi falala, Allah Madaukakin Sarki ya rantsuwa da su a cikin Alkur’ani. Manzon Allah (SAW) ya ce ba wani aiki na alheri da ya fi so ga mutum ya yi cikin shekara kamar yawaitar ibada a cikin wadannan kwanaki.”
Ibn sina ya yi nuni da abubuwan da ake so Musulmi ya yi a wannan lokaci, ciki har da:
Yawaitar salati, istigfari, hailala da karatun Alkur’ani
Yin nafiloli da azumi, musamman ga wadanda ba za su yi aikin Hajji ba
Sadar da zumunci da bayar da sadaka
Ya kara da cewa, “Ana so Musulmi su yi azumi a cikin kwanakin goma, sai dai wadanda za su tafi Hajji kada su yi azumin ranar Arafah, kuma wadanda ba za su yi ba su daina azumi a ranar Sallah, wato cikon goman watan.”
Mai halin yin Layya
ya kuma shawarci al’umma masu karfin yin layya da su kiyaye kada su yi aski ko yanke faratansu a cikin wannan lokaci, domin bin koyarwar Sunnah.












