DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Wasu malamain addinnin Musulunci dana Kirista sun koka akan Gwamnatin Tarayya, domin sanya hannu akan Yar-je-je-ni-yar,
A cewarsu, yarjejeniyar tana dauke da wasu sharadai da suka kunshi cewa kasashe masu tasowa dole su yarda da ‘yancin ‘yan luwadi da ‘yan madigo da kuma ‘yancin yin auren jinsi daya in da suka bayyana rashin jindadinsu
Bayanai akan yarjejeniyar ya fito ne lokacin da Ministan Kasafin Kudi Da Tattalin Arziki Alhaji Abubakar Atiku Bagudu, ya bayyana irin halin da ake samu a wata liyafa da kungiyar Kasashen Turai suka shirya a Abuja. Duk da dai ya ce, Najeriya ta sa hannu ne a sahale bashin Dala Billiyan 150.
Kasashe da dama a duniya sunke yadda sun sanya hannu kan yarjejeniyar a 2023 lokacin da aka yi ta. Kasashe sun hada da: Guinea, Trinidad, Tobago, Mauritania da wasu Kasashen Afrika da dama
Yanzu haka wannan lamari ya jawo cece-kuce a shafukan sada zumunta na Najeriya inda ‘yan Najeriya ke nuna allawadai da wannan lamarin.












