DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Mahaifiyar fitaccen mawakin siyasar nan Dauda Kahutu Rarara Hajiya Hauwa’u Adamu, ta sami ‘yanci bayan shafe kwanaki 20 a hannun masu garkuwa da mutane.
Duk da har yanzu babu cikakken bayanin yadda aka sako dattijuwar mai kimanin mai shekaru 75, amma rahotannin da ba a tabbatar da su ba sun ce an biya wasu makudan kudade a matsayin kudin fansa kafin a Sako dattijuwar.
Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito an sace mahaifiyar mawaki Rarara ne a jihar Katsina a cikin watan da ya gabata.












