DAGA: HASSANB UMAR GWAMMAJA
An ware ranar ne domin duba batutuwan da suka shafi masu bukata ta musamman, da nufin yin gangamin tallafa masu ta fuskar kare mutunci da hakkokinsu, da kuma kyautata halin rayuwarsu
Ana amfani da wannan rana don fadakar da sauran al’ummar duniya game da muhimmancin damawa da masu bukata ta musamman a daukacin al’amuran rayuwa, kamar siyasa da zamantakewa da tattalin arziki da al’adu da dai sauransu.
Sai dai a Najeriya, wasu masu bukatar ta musamman sun ce wannan rana ta bana ta zo musu da kalubale daban-daban, da nasarori har ma da matsaloli.
Dakta Micah shabi, shi ne shugaban kungiyar cigaban da wayar da kain masu bukata ta musammam na jihar Kaduna ya bayyana cewa suna farin ciki da wannan rana, sai dai ba’a kolawa da masu bukata ta musammam a Najeriya
“Akwai damuwa kwarai da gaske ga masu bukata ta musamman domin ba sa samun kulawar da ta dace,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, ”babban ƙalubalen da suke fuskanta na rayuwa shi ne rashin tsaro da ya tarwatsa al’ummar arewa abin da ya janyo su kansu masu bukata ta musamman din ba sa samun kulawar da ta dace.”
Shi ma Malamin addinin musulunci nan dake a jihar Kaduna, Dakta Muhammed Nuraini Ashafa, ya yi kira da jan hankale shugaban da masu hannun da shuni su rika taimakawa masu bukata ta musammam
Amma malamin ya sake yin kira ga masu bukata ta musamman su rika sanya wa a ransu cewa kamar kowanne mutum babu abin da zai gagare su koda kuwa suna da wata nakasa, su cire shakku suna jajircewa in ji shi.
Tun a shekarar 1976 Majalisar Ɗinkin Duniya ta ayyana 1981 a matsayin shekarar masu bukata ta musamman, inda kuma aka fara bikin ranar daga 3 ga watan Disamba 1992.
Take Ranar na baba shi ne; A baiwa masu bukata ta musammam hakinsu !












