• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Cutar mashako

Khadija Maitaya by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Reading Time: 1 min read
0
Home LAFIYA
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Date:1stSep
By Khadija Muhammad Maitaya

Akalla mutane 1,000 ne suka kamu da cutar mashako a ƙananan hukumomi 26 na Jihar Katsina cikin watanni takwas da suka gabata.

RelatedPosts

Governor Yusuf commissions Kano center for disease control

Shirin Gwamnatin Kano Na Kula Da Lafiyar Baki Ya Amfanar Da Mutane sama da 15,000

An Kama Wata Matashiya Mai Shekaru 27 Bisa Zargin Satar Jariri A Asibiti A Zamfara

Sakataren Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta jihar, Dakta Shehu Kabir, ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai kan halin da cutar ke ciki a jihar.

Ya ce akwai alamun cewa kusan kashi biyar cikin 100 na mutanen da suka kamu da cutar sun rasa rayukansu, sai dai ya ce wannan adadi na buƙatar ƙarin bincike domin tabbatar da sahihancinsa.

Dakta Kabir ya ce ƙananan hukumomin Funtua, Kankiya, Bakori, Katsina, Mashi da Daura na daga cikin wuraren da aka fi samun masu fama da cutar.

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakan gaggawa domin dakile yaɗuwar cutar, ciki har da gudanar da allurar rigakafi a ƙananan hukumomin Bakori, Charanchi, Funtua, Mashi da Kankiya.

A cewarsa, an kuma kafa cibiyoyin kula da masu fama da cutar guda uku a biranen Katsina, Funtua da Daura, domin ba da kulawar gaggawa ga waɗanda suka kamu da ita.

“Gwamnati ta kuma samar wa jami’an lafiya magungunan da ake buƙata domin kula da masu fama da cutar,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa an horas da jami’an lafiya kan hanyoyin sa ido, gano masu kamuwa da cutar, ɗaukar matakan gaggawa da kai rahoton bullar cutar domin a samar da kulawa cikin lokaci.

Cutar mashako na iya haifar da matsalar numfashi, bushewar makogaro da zazzabi.

Dakta Kabir ya yi kira ga hakimai, dagatai da masu unguwanni da su taimaka wa jami’an lafiya wajen wayar da kan al’umma, musamman iyaye, kan muhimmancin kai yara wuraren da ake gudanar da allurar rigakafin cutar..

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Khadija Maitaya

Khadija Maitaya

RelatedPosts

Governor Yusuf commissions Kano center for disease control
LAFIYA

Governor Yusuf commissions Kano center for disease control

by Khadija Maitaya
August 4, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Ginin da Ya Janyo Ce-ce-ku-ce a Unguwar Dorayi, Kano
LAFIYA

Shirin Gwamnatin Kano Na Kula Da Lafiyar Baki Ya Amfanar Da Mutane sama da 15,000

by Khadija Maitaya
July 22, 2026
An Kama Wata Matashiya Mai Shekaru 27 Bisa Zargin Satar Jariri A Asibiti A Zamfara
LAFIYA

An Kama Wata Matashiya Mai Shekaru 27 Bisa Zargin Satar Jariri A Asibiti A Zamfara

by aksam
May 17, 2026
Najeriya Sama Da 4,600 Ne Suka Koma Kasashen Waje Da Aiki A Cikin Shekaru 3 ‎ ‎—Rahoto
LAFIYA

Najeriya Sama Da 4,600 Ne Suka Koma Kasashen Waje Da Aiki A Cikin Shekaru 3 ‎ ‎—Rahoto

by aksam
April 22, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Ƴan sanda sun ƙwato yarinya ƴar shekara 12 da aka Daura wa aure da mai sheka 63

Ƴan sanda sun ƙwato yarinya ƴar shekara 12 da aka Daura wa aure da mai sheka 63

April 2, 2024
Innallillahi  Wa’innailahir  Rajiun!!! Allah Ya Ji Kan Alhaji Kabiru Sanda

Innallillahi Wa’innailahir Rajiun!!! Allah Ya Ji Kan Alhaji Kabiru Sanda

May 10, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media