• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Daukar DanKwankwaso Ya Zama Dan Takarar Mataimakin Gwamnan Kano A NDC Ya Jaho Ce-ce-ku-ce

aksam by aksam
June 16, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home SIYASA
ADVERTISEMENT
465
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga: Hassan Umar Gwammaja

Dan takarar gwamnan Jihar Kano na jam’iyyar NDC a zaben shekarar 2027, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya bayyana Hon. Mustapha Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin abokin takararsa.

RelatedPosts

An Kona Fastocin Peter Obi Da Kwankwaso A Jihar Kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

An sanar da hakan ne a ranar Litinin bayan gabatar da Hon. Mustapha Kwankwaso a gaban kwamitin koli na jam’iyyar da sauran masu ruwa da tsaki a wani taron da aka gudanar a Miller Road da ke Kano.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun dan takarar gwamnan, Ibrahim Garba Shuaibu, ya fitar, ya bayyana cewa zaben Hon. Mustapha Kwankwaso ya biyo bayan nazari mai zurfi da tuntuba da aka yi, domin karfafa manufar jam’iyyar, da hadin kan jam’iyyar NDC.

Sanarwar ta ce an zabi Hon. Mustapha Kwankwaso ne bayan tattaunawa da tuntuba da aka yi da bangarori daban-daban tare da yin la’akari da wasu fitattun mutane da suka cancanta.

Kotun Tarayya Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu Hudu

Da yake magana kan wannan ci gaba, Kwamared Gwarzo ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa abokin takararsa zai taka muhimmiyar rawa wajen aiwatar da manufofin gwamnatinsu idan suka samu nasara, yana mai cewa kwarewarsa, nagartar shugabanci da kuma karbuwarsa a tsakanin al’umma sun sanya shi zama babban jigo a wannan tikitin takara.

Hon. Mustapha Kwankwaso, wanda tsohon Kwamishinan Matasa da Wasanni ne na Jihar Kano, ya shahara wajen hidimtawa jama’a tare da bayar da gudunmawa a bangaren bunkasa matasa da ayyukan ci gaban al’umma.

Sanarwar ta kara da cewa jam’iyyar NDC ta yi imanin cewa hadakar Gwarzo da Kwankwaso na kunshe da kwarewa, gogewa, amana da jajircewar da ake bukata domin magance kalubalen da ke fuskantar Jihar Kano tare da samar da shugabanci nagari ga al’ummar jihar.

Mustapha dai shi ne Babban da ga jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabi Musa Kwankwaso .

Share186Tweet116SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Rundunar Sojin Najeriya Ta Yi Nasarar Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane

Next Post

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

aksam

aksam

RelatedPosts

An Kona Fastocin Peter Obi  Da  Kwankwaso  A Jihar Kano
SIYASA

An Kona Fastocin Peter Obi Da Kwankwaso A Jihar Kano

by aksam
June 1, 2026
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma  Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC)  A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar
SIYASA

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

by aksam
May 3, 2026
Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Umarci  Duk Masu Riƙe Da Mukaman Siyasa Dake Da Niyyar Tsayawa Takara Dasu Yi Murabus Kafin Ranar Juma’a 24 ga Watan Afrilu 2026
SIYASA

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

by aksam
May 2, 2026
Ba Za Mu Bawa Kwankwaso Tikitin Takarar Shugabancin Kasa A Jam’iyyarmu— NNPP
SIYASA

Wasu Dalilin Da Suka Sa Kwankwaso Ke Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar ADC

by aksam
May 2, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Τεχνικές και πρακτικές για ταχεία ανάληψη σε online καζίνο

April 21, 2025
Jawabin Tinubu ya ja hankalin shugabannin Africa su tausaya wa al’ummar su

Shugaba Bola Tinubu, Ya Amince Wa Kamfanin Man Fetur Na Ƙasa (NNPCL), Da Ya Yi Amfani Da Ribar Shekarar 2023 Da Aka Mamu Domin Biyan Tallafin Man Fetur.

August 19, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media