• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

An Yi Mummunar Faɗuwa a Sakamakon Jarrabawar Bana – WAEC

aksam by aksam
August 5, 2025
Reading Time: 3 mins read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

RelatedPosts

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka

Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano

Daga Hassan Umar Gwammaja,
Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana cewa an samu gagarumar faduwa a sakamako da aka fitar na jarrabawar WASSCE na wannan shekara ta 2025, idan aka kwatanta da ta bara.

Daga cikin dalibai 1,969,313 da suka rubuta jarabawar a makarantu 23,554, Dlibai 754,545 ne suka samu akalla credits guda biyar ciki har da Turanci da Lissafi — wato kashi 38.32% — . Wannan na nuna raguwar kashi 33.8% idan aka kwatanta da kashi 72.12% da aka samu a shekarar 2024.

A yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a hedkwatar WAEC dake Yaba, Legas, ranar Litinin 4 ga Agusta 2025, shugaban ofishin WAEC na kasa, Dr. Amos Dangut, ya danganta wannan koma baya da sabon tsarin da WAEC ta bullo da shi na nuna bambancin takardun jarrabawar objective a muhimman darussa kamar Turanci, Lissafi, Biology da Economics.

“Wannan tsari ya rage yawaitar hadin baki da aikata magudi a jarabawa. Mun lura da raguwar sakamako a bangaren objective, amma sakamakon essay bai canza sosai ba. Wannan wani karfi ne na nuna cewa dalibai su maida hankali wajen shiri da kansu,” in ji Dangut.

An gudanar da jarrabawar daga 24 ga Afrilu zuwa 20 ga Yuni, 2025, yayin da aikin duba sakamako ya gudana daga 3 zuwa 21 ga Yuli. WAEC ta kuma yi amfani da sabon tsarin lissafi na zamani kai tsaye domin hanzarta fitar da sakamako cikin lokaci.

Daga cikin yawan daliban da suka rubuta, 1,517,517 (wato kashi 77.06%) sun samu sakamakon su cikin koshin lafiya, yayin da sakamakon 451,796 (kashi 22.94%) ke kan aiki saboda matsalolin fasaha. WAEC ta tabbatar da cewa za a warware matsalolin cikin ‘yan kwanaki masu zuwa.

Game da magudin jarrabawa, 192,089 daga cikin sakamakon — wato kashi 9.75% — an dakatar da su saboda laifuffuka irin su amfani da wayoyin hannu da aka haramta da kuma hadin baki. Wannan adadin bashida yawa idan aka kwatanta da kashi 11.92% da aka dakatar a 2024.

“Wadanda ke aikata wadannan laifuka suna zama kalubale a gare mu. Wasu ma har suna amfani da sunan WAEC suna yada labaran bogi. Mun kama wasu, kuma hukunci ya wajaba a kansu,” in ji Dangut.

Dangut ya kuma ce jihohin da ake bin su bashi ba za su iya samun sakamakon daliban da suka dauki nauyin su ba har sai sun biya bashi.

A bangaren daliban da ke da bukatu na musamman, 12,178 ne suka yi rajista. Daga ciki, 112 na fama da rashin gani, 615 na da matsalar kunne, 52 na da matsalolin kwakwalwa, sai kuma 37 masu nakasa ta jiki. WAEC ta tabbatar da cewa an ba su dukkanin kulawa ta musamman da ake bukata.

Dangane da jinsin dalibai, 976,787 (wato kashi 49.60%) maza ne, yayin da 992,526 (kashi 50.40%) mata ne.

Daga cikin 754,545 da suka samu credits guda biyar da suka hada da Turanci da Lissafi, mata sun fi maza da kashi 53.99% (407,353), yayin da maza suka kasance kashi 46.01% (347,192).

An fitar da sakamakon ne a hukumance ranar Litinin ta shafin WAEC na X (Twitter). Inda aka umarci Dalibai da su ziyarci http://waecdirect.org domin ganin sakamako.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Innalillahi Wa’inallaihir Rajun Allah Ya Jikan Abbati Isah (Babba)

Next Post

Kwamishinan Harkokin Sufuri na Kano Ya Ajiye Aiki Saboda Cece-kucen Zargin karbar Belin Wanda Ake Zargi da Dillancin Miyagun Kwayoyi

aksam

aksam

RelatedPosts

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi  Annabi Muhammadu SWA  A Garin Nkawkawo
Uncategorized

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

by aksam
September 1, 2026
Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka
Uncategorized

Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka

by aksam
August 26, 2026
Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano
Uncategorized

Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano

by aksam
August 26, 2026
Gwajin DNA: Kashi 23.6% Na Gwaje-Gwajen Uba A Najeriya Sun Nuna Rashin Daidaito
Uncategorized

Gwajin DNA: Kashi 23.6% Na Gwaje-Gwajen Uba A Najeriya Sun Nuna Rashin Daidaito

by aksam
August 25, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Kalli shirin da ake na mayar da fadar mulkin Nageriya Legas

Rundunar Yan sanda tayi shagube ga maauratan dake fuskantar cin zarafi a gidajen aurensu

July 4, 2024
Gwamnati Tinibu ta sahale wa gwamnoni kirkirar yansandan jihohi amma bisa sharadi 1 tak

Gwamnati Tinibu ta sahale wa gwamnoni kirkirar yansandan jihohi amma bisa sharadi 1 tak

February 16, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media