YANZU-YANZU: Yan sanda a Iran sun sami Nasarar kama ƴan leken asirin Isra’ila.
Rundunar ‘yan sanda iran, ta ce ta kama wasu jami’an leƙen asiri guda biyu na Mossad a lokuta dabam-dabam, tare da kwace makamai da kayan fashewa masu yawa.
Sa’eed Montazer al-Mahdi, mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda ta Jamhuriyar Musulunci ta Iran, ya bayyana a ranar Lahadi cewa an gano kuma an kama jami’an guda biyun ne a unguwar Fashafuyeh, da ke cikin ƙaramar hukumar Ray a lardin Tehran.
Montazer al-Mahdi ya ce an kwace fiye da kilo 200 na abubuwan fashewa, da kayan sarrafa jiragen yaki marasa matuki guda 23, da makaman harba su (launchers), da sauran kayan aikin yaki daga hannun su. Haka kuma, an kama wata mota kirar Nissan pickup.











