NLC ta bukaci ‘yan sanda su karkata bindigoginsu zuwa kan ‘yan ta’adda, maimakon masu zanga zanga
Kungiyar kwadago a Najeriya ta bukaci ‘yan sanda da su karkata bindigogin su zuwa kan ‘yan ta’adda maimakon masu zanga zangar lumana.
Shugaban kungiyar Joe Ajaero ne ya bayyana haka, yayin da yake kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya kawo karshen wadannan matsaloli da suka addabi jama’a da kuma biyan bukatun masu zanga zangar.
Ajaero yace hanya guda ta warware wannan matsalar ta zanga zanga itace ta hanyar tattaunawa da shugabannin ta, maimakon barazanar da ‘yan sanda da kuma sojoji ke yi.
Shugaban yace sakamakon samun shaidun dake nuna cewar mutane sama da 40 sun mutu, ya zama wajibi su tuhumi yadda jami’an tsaron ke gudanar da ayyukan su.
Premium Times ta ruwaito Ajaero yace da ‘yan sanda sun yi amfani da irin wannan karfin da ake bukata wajen kai hari a kan ‘yan bindiga da kuwa an shawo kan matsalar tsaron da ake fuskanta. Shugaban ya bayyana damuwar kungiyar su dangane da asarar rayuka da kuma dukiyoyin da aka samu.
Premium Time











