Hukumar hisbah ta jihar Kano ta nanata kudurinta na cika alkawarin sabon gwamnan Kano injiniya Abba Kabir Yusuf na ci gaba da gudanar da auren zawarawa a jihar Nan.
Babban kwamandan hukumar sheik Aminu Ibrahim daurawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai a dai dai lokacin da yake kama aiki a hukumar biyo bayan karbar takardar kama aikin sa hukumar Jim kadan bayan dawowar sa daga kasa Mai tsarki bayar gudanar da aikin hajji.
Idan za,a iya tunawa lamarin nadin shehin malamin ya Dade ana tattaunashi a kafafen sada zumunta da sauran wuraren da mutane ke haduwa dama
ita kanta hukumar hisbah tun kafin samun mikawa malamin takardar kama aiki a matsayin kwamandan hisbah na jihar Kano .sheik Daurawa yace ba zasuyi kasa a gwiwa ba wajen bin umarnin gwamnati na aurad da zawarawa da yammata a fadin jihar kano.
Sheik Aminu Daurawa yace bazasu laminci cin amanar gwamnati ba a wannan karon domin a baya an Sami wasu bata garin da suke zuwa a matsayin zawarawa alhalin sun Dade a tare a matsayin ma,aurata don haka yace a wannan karon bazasu laminci wannan zamba cikin amincinba
Ya kuma Kara da cewa a bangaren kayan dakin da ake bawa ma,auratan da suka samu shiga auran zawwarawa anyi tsari domin har kwamati aka kafa Wanda zai sa idanu a Samar da ingantattun kayan ta inda duk Wanda aka bawa kwangila yayi almundahana ba zasu kyale shi ba.
Kwamandan ya ce sun shiya tsaf domin tunkarar gudanar da auran zawarawa Nan ba da dadewaba.
A wani cigaban kuma Wakiliyar mu Jamila Sulaiman Aliyu, ta labarta Mana cewa kwamandan yaja hankalin dakarun hukumar dasu dage wajen zamarwa al’ummar Kano ababan kwatance tun daga fuskar ibada zuwa muamala Mai kyau domin su madubi nee ga al’ummar da suke tare dasu.












