Daga Hassan Umar Gwammaja
Kakakin rundunar yan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanrwar da fitar a ranar Alhamis, a madadin kwamishinan yan sandan jahar CP Salman Dogo Garba.
Sanarwar ta ce rundunar ta yi duba na musamman akan korafe-korafen da ake samu na kisan kai , wanda daga fada sai a chakawa mutum wuka ko kuma tsintar gawar da ruwa ya cinye.
SP Abdullahi kiyawa , ya kara da cewa , wadannan abubuwa suna sanya al’umma cikin damuwa, wanda ya zamo dole a kara sanya ido kan yaya, yara , matasa don nusar da su kan matsaloli.
Cikin shawarwarin da rundura ta bayar sun hada da, a guji duk wani fada ko hada jiki don kaucewa abun da zai haifar da riciki da rigima, haka zalika a guji daukar wani makami da suka hada da Wuka, Gora, Fashasshiyar Kwalaba da kuma karafa.











