Ƙwamishinan ƴan sanda na Jihar Katsina ya bayyana hakan ne a wani zama da akayi na masu ruwa da tsaki da kuma Gwamnatin Jihar Katsina inda yace:
“Jami’an hukumar ƴan sanda a shirye suke wajen bada tsaro ga mutanen da zasu shirya zanga zangar matuƙar suka cika sharuɗan da hukumar ta tanada, na aikawa sunansu da sauran mutanen da zasu Jagoranci zanga-zangar”
A ɓangare ɗaya suma shugabannin ƙungiyoyin da suka nuna rashin goyon bayan gudanar da zanga-zangar sun bayyanama Gwamnati dalilansu akan janyewar.
Mai girma muƙaddashin Gwamnan jihar Katsina Mal. Faruk Lawal Joɓe, yayi ganawa ta musamman da shugabannin ƙungiyoyin, ƴan kasuwa, direbobi, masu gidajen mai da sauran ƙungiyoyin fararen hula na matasan jihar Katsina da suka nuna rashin goyon bayansu akan zanga-zanga da ake ƙoƙarin gudanarwa a faɗin ƙasar nan.
Yayin ganawar muƙaddashin Gwamna Mal. Faruk Lawal Joɓe ya bayyana mutane jihar Katsina a matsayi masu ƙaunar zaman lafiya da biyayya ga umarnin Gwamnati, bayan haka yayi ƙarin haske aka wasu daga cikin shirye shirye na taimakawa al’umma da kayan abinci tare da jari da Gwamnatin jihar Katsina haɗin gwaiwa da gwamnatin tarayya suka shirya a lokuttan baya a ƙoƙarin Gwamnati na kawoma al’umma sauƙi, da kuma irin matakan da yanzu Gwamnatin ke dauka wajen fiddo da tsare tsare da zasu ragema al’ummar jihar Katsina raɗaɗin tsadar kayan masarufi da ake fama dashi a ƙasar nan, domin ganin sun samu sauƙin rayuwa musamman akan al’amuran da suka shafi tsadar kayan masarufi da kawon ƙarshen matsalar tsaro a jihar Katsina.
Ganawar ta samu halartar, shugaban majalissar dokoki, Rt. Hon Nasir Yahaya Daura, shugaban ma’aikata na gidan Gwamnatin jihar Katsina, Hon. Jabiru Salisu Abdullahi, ƙwamishinoni, chiyamomin ƙananan, ƴan majalissar dokoki, shugaban Jami’an tsaro na farin kaya, shugaban sojoji, ƙwamishinan ƴan sanda, shugaban hukumar kiyaye haɗurra, da sauran manyan jami’an Gwamnatin da ƙungiyoyin matasa.











