DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Masu zanga zangar sun fantsama kan tituna a jihar ta Naija dauke da kwalaye ,inda suke kira da a kawo karshen tsadar rayuwa,wasu nacewa halin kunci da aka jefa talaka a ciki ya isa haka.
Wasu Kuma sun rubuta cewa dole ne a dawo da tallafin man fetur a Najeriya.
Rahotonni na cewa, dama tun tuni wasu sun fitar da sanarwar cewa ,za su fara Zanga-zangar ne daga ranar 29 ga Watan Yuli yayin da wasu kuma zasu fara daga 1 ga watan Agusta.












